MANUFAR OSINBAJO NASAN ZAMA SHUGABAN KASA 2023.
Farfesa Farooq Kperogi Ya Sake Ban kado Wasu Boyayyun Manufofi Na Farfesa Yemi Osinbajo Akan Musulunci
Osinbajo a jawabinsa na tsayawa takarar shugaban kasa, yace yana son idan ya zamo shugaban kasa a samu Nigeria guda daya, al’umma daya, babu bambancin addini ko yare ko yanki ko kabila.
Don haka Kperogi ya ce to bari mu gani shin wannan alkawarin da gaske ne? A dubi abinda Osinbajo ya yi a iya kasancewarsa Mataimakin Shugaban Kasa na shekaru 7:
Duk mukaman da Osinbajo ya rike a rayuwarsa ta siyasa a dalilin Musulmi ne, amma shi duk mukamin da ya samu dama Memba na kungiyarsu ta Redeemed Christian Church of God ya ke bawa, kuma mafi yawanci Pastoci.
1. A 2015, an bashi damar zabar Minista, sai ya gabatar da Okechukwu Enelamah, Pastor na RCCG, wanda aka bawa Minister na Industry, Trade & Investment har zuwa 2019.
2. Mai magana da yawunsa, Laolu Akande, Pastor ne na RCCG.
3. Shi ke jagorantar tattalin arzikin kasar, dukkan manyan mukamai na tattalin arziki Pastocin RCCG ya bawa.
4. A lokacin da aka bukaci ya nada Chairman na Federal Inland Revenue Service (FIRS) sai ya zabi Babatunde Fowler, Pastor na RCCG.
5. Director General na Bureau of Public Enterprises (BPE), nan ma ya nada Pastor na RCCG mai suna Alex Ayoola Okoh.
6. A lokacin da aka bukaci nada MD na Nigeria’s Bank of Industry (BOI), Osinbajo ya nada Pastor na RCCG mai suna Olukayode Pitan wanda ya maida hukumar ta BOI Cocin RCCG.
7. Bai tsaya a iya mukaman gwamnati ba, yana amfani da damarsa wajen nada yan kungiyarsu ta RCCG hatta a shugabancin jami’o’i a kasar Yarbawa kamar nada Pastor na RCCG a matsayin Soun na Ogbomoso.
8. Wannan itace manufarsa kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito ya fadawa shugabannin Kiristoci a Lagos a ranar 4/November/2016 cewar matsayinsa na Mataimakin Shugaban Kasa ITACE DAMARMU (SHUGABANNIN KIRISTOCI) TA FARKO. KUMA MUNA BUKATAR FADADA WANNAN DAMAR MU YI IYA IYAWARMU. ZABATA YA BUDE MANA KOFA.
A karshe Farfesa ya ce in wannan ne abinda yan Nigeria ke bukata to Allah