Labarai

FARIN CIKIN YAN NIGERIA.

Majalisar Dattawa da ‘yan majalisar wakilan Nigeria sun amince a bawa kananan hukumomin Nigeria ‘yancin cin gashin kansu daga Gwamnonin jihohin Nigeria

Majalisa ta amince kamar yadda Gwamna yake da ‘yancin a zabeshi yayi shekara 4 ko 8 idan ya zarce yana mulki to haka aka bawa shugabannin kananan hukumomi wannan ‘yancin, sai kuma ‘yancin mallakar kudin karamar hukuma

‘Yan majalisun tarayyar Nigeria 258 suka amince da a bawa kananan hukumomi ‘yanci, yayin da ‘yan majalisu 15 ne kacal suka ki amincewa

A bangaren Majalisar Dattawa, Sanatoci 92 ne suka amince a bawa kananan hukumomi ‘yanci, Sanatoci 2 ne kacal suka ki amincewa

Majalisa tayi doka kowace karamar hukuma a Nigeria za’a bude mata account number wanda za’a dinga tura kudin kananan hukumomi kai tsaye daga Gwamnatin tarayya, wato an datsewa Gwamnoni ikon mallakar kudin kananan hukumomi ta kowace hanya

Wallahi wannan matakin da Gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari ta dauka ba karamin tasiri da amfani zai yiwa talakawa ba, yanzu ne talakawan Nigeria zasu fara cin moriyar tsarin mulkin Demokaradiyyah

Shugaba Buhari da duk wanda yake da hannu wajen bawa kananan hukumomi ‘yanci Allah Ya saka musu da alheri

arewanahiya

Farin cikinmu shine ganin farin ciki saman fuskarku muna alfahari duku masoya.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button