Labarai

YAN SANDAN NIGERIA SUNYI NASARAR CHAFKO WANI MUTUN DA,AKE ZARGI BATA GARI CIKIN LAUYOYI.

Rundunar ‘yan-sandan Najeriya tayi awaon gaba da wani mutum da ake zargi lauya ne na bogi da ya dau tsawon lokaci yana waklitar jama’a a kotu a jihar Zamfara.

Rundunar ta gabatar da Chukwuka Jude mai shekara 46 a wani taron manema labarai da kakakinta SP Mohamaed Shehu ya jagoranta a hedikwatarta a Gusau, ranar Litinin din nan 24 ga Janairun, 2022.

Kayayyakin da aka samu a wurin mutumin wadanda rundunar za ta gabatar a matsayin sheda sun hada da, katin shedar aiki na bogi da stamfi da kuma takardun rubuta wasika da ke dauke da sunan kamfaninsa na aikin lauya ; J.N Monyei & Co. Chamber.

A jawabin kakakin ‘yan-sandan ya ce a ranar 18 ga watan nan na Janairu ne 2022, shugaban kungiyar lauyoyi na jihar Zamfara ya gabatar wa da ‘yan sanda kara cewa, a wannan rana an kama wani mutum a cikin Babbar Kotun Shari’a da ke Tudun Wada a Gusau yana gabatar da kansa a matsayin lauya ga wani.

Nan da nan kuma masu bincike na ‘yan-sanda suka shiga aikinsu inda suka nasarar chaf ko mutumin, wanda a yanzu yake hannu yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike.

Binciken farko-farko yan una cewa mutumin ya dau tsawon lokaci yana gabatar da kansa a matsayin lauya a kotuna da dama na jihar da suka hada da a kananan hukumomin

Kauran Namoda da Birnin Magaji da Shinkafi kuma Gusau da dai sauran su inda a karshe aka kama shi yana wakiltar wani da ya karbi kudi a wurinsa yana wakiltarsa a matsayin lauya.

Rundunar ta ce mutumin da ake zargi a kokarins ana tsere wa kamu da shari’a ya yi tayin bai wa dan sandan kotu cin hancin naira dubu dari uku, wanda jami’in ya ki karba.

arewanahiya

Farin cikinmu shine ganin farin ciki saman fuskarku muna alfahari duku masoya.

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button